fidelitybank

An harbe ‘yan bindiga biyu tare da kubutar da wani a Katsina

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina a ranar Laraba, ta ce, jami’anta sun kashe ‘yan bindiga biyu tare da kubutar da wani da aka yi garkuwa da su.

‘Yan sandan sun kuma fatattaki ‘yan bindiga da dama a wasu kauyuka biyu.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan, SP Gambo Isah, a cikin wata sanarwa da ya fitar, ya ce rundunar ta samu kiran gaggawa ne a ranar 12 ga watan Fabrairun 2023, da misalin karfe 04:45, inda ‘yan ta’addan suka kai farmaki a kauyen Kitibawa. Karamar hukumar Dutsinma tare da yin garkuwa da wani Alhaji Ado Rumawa.

Karanta Wannan: Buhari ya yi Allah wadai da harin jihar Katsina

Ya ce nan take kwamandan yankin na Dutsinma ya jagoranci tawagar ‘yan sanda da ke sintiri zuwa yankin, inda suka yi artabu da ‘yan ta’addan, inda ya ce rundunar ta samu nasarar fatattakar ‘yan ta’addan inda aka kashe daya daga cikinsu.

A cewarsa, an kubutar da wani da aka yi garkuwa da shi ba tare da jin rauni ba yayin da da yawa daga cikin ‘yan ta’addan suka gudu da raunukan harbin bindiga.

Ya yi bayanin cewa jami’ai da mazaje na kan hanyarsu ta zuwa wurin, domin kamo sauran ‘yan bindigar da suka jikkata

“An kashe wani dan ta’adda a hanyar Danja zuwa Bakori, “a daidai wannan rana da misalin karfe 01:35, an samu kiran gaggawa cewa wasu ‘yan ta’adda kimanin 20 dauke da muggan makamai sun tare hanyar Danja zuwa Bakori, suna fashin fasinjojin da ba su ji ba ba su gani ba. Unguwan Balarabe junction.

“Rundunar ta Danja ta jagoranci tawagar ‘yan sanda zuwa yankin inda suka yi artabu da ‘yan bindigar.”

today daily post news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp