Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina a ranar Laraba, ta ce, jami’anta sun kashe ‘yan bindiga biyu tare da kubutar da wani da aka yi garkuwa da su.
‘Yan sandan sun kuma fatattaki ‘yan bindiga da dama a wasu kauyuka biyu.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan, SP Gambo Isah, a cikin wata sanarwa da ya fitar, ya ce rundunar ta samu kiran gaggawa ne a ranar 12 ga watan Fabrairun 2023, da misalin karfe 04:45, inda ‘yan ta’addan suka kai farmaki a kauyen Kitibawa. Karamar hukumar Dutsinma tare da yin garkuwa da wani Alhaji Ado Rumawa.
Karanta Wannan: Buhari ya yi Allah wadai da harin jihar Katsina
Ya ce nan take kwamandan yankin na Dutsinma ya jagoranci tawagar ‘yan sanda da ke sintiri zuwa yankin, inda suka yi artabu da ‘yan ta’addan, inda ya ce rundunar ta samu nasarar fatattakar ‘yan ta’addan inda aka kashe daya daga cikinsu.
A cewarsa, an kubutar da wani da aka yi garkuwa da shi ba tare da jin rauni ba yayin da da yawa daga cikin ‘yan ta’addan suka gudu da raunukan harbin bindiga.
Ya yi bayanin cewa jami’ai da mazaje na kan hanyarsu ta zuwa wurin, domin kamo sauran ‘yan bindigar da suka jikkata
“An kashe wani dan ta’adda a hanyar Danja zuwa Bakori, “a daidai wannan rana da misalin karfe 01:35, an samu kiran gaggawa cewa wasu ‘yan ta’adda kimanin 20 dauke da muggan makamai sun tare hanyar Danja zuwa Bakori, suna fashin fasinjojin da ba su ji ba ba su gani ba. Unguwan Balarabe junction.
“Rundunar ta Danja ta jagoranci tawagar ‘yan sanda zuwa yankin inda suka yi artabu da ‘yan bindigar.”