Mutum aƙalla shida ne aka kashe tare da raunata wasu 10 sakamakon harbe-harbe a Sacramento da ke Amurka, a cewar ‘yan sandan California.
Mutane sun fara neman gidan ɓuya daga kan titi bayan sun ji ƙarar harbi daga yankin da ke cike da gidajen cin abinci da na shan giya a yau Lahadi.
‘Yan sandan suna shawartar mazauna yankin da su ba ta duk wasu bayanai da suka sani da zai taimaka wajen gano maharan. In ji BBC.
Shugaban ‘yan sandan Sacramento Katherine Lester ta faɗa wa manema labarai cewa ‘yan sanda da ke kusa da yankin da lamarin ya faru sun ji ƙarar harbe-harbe da misalin ƙarfe 2:00 agogon ƙasar – 10:00 agogon Najeriya da Nijar.
“Wannan bala’i ne mai girma,” a cewarta.