fidelitybank

An harbe Baturan ‘Yan Sanda da mutane 5 a Benue

Date:

Wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba da ake zargin ‘yan ta’adda ne, sun kashe Baturan ‘yan sanda reshen Naka, Mahmud Abubakar, a jihar Benue.

Rahotanni sun nuna cewa, maharan sun kai wa Sufeton ‘yan sandan hari ne a ranar Talata a lokacin da yake dawowa daga Makurdi, inda ya je yi wa rakiyar zaman lafiya.

Naka hedikwatar karamar hukumar Gwer ta yamma ce a jihar Benue, inji rahoton Naija News Hausa.

Jaridar PUNCH ta rawaito wata majiya na cewa harin ya faru ne da misalin karfe 3:30 na yammacin jiya. Da yake tabbatar da faruwar lamarin, kwamishinan ‘yan sandan jihar Binuwai, Wale Abbas, ya shaida wa manema labarai ta wayar tarho cewa an yi wa dan sandan kwanton bauna ne a lokacin da yake komawa ofishinsa.

Ya ce, “Gaskiya ne an kashe DPO; yaje rakiya ne suka share masa hanya. Akan hanyarsa ta zuwa Naka suka yi masa kwanton bauna.”

Karanta Wannan: Baturen ‘yan sanda a Jigawa ya rasu a ofishin sa

An tattaro daga ranar Lahadi zuwa Talata, akalla wasu mutane biyar wasu da ake zargin makiyaya ne suka kashe a wasu al’ummomin da ke majalisar.

A halin da ake ciki, Shugaban karamar hukumar Gwer West, Ayande Andrew, ya yi ikirarin cewa makiyaya ne suka kashe DPO.

Ya ce, “Makiyaya ne suka tare hanyar kuma DPO na kan hanyarsa ta zuwa Makurdi ne suka yi masa kwanton bauna; shi kadai ne a cikin motar da ke kan hanyar.”

A kan sauran biyar da aka kashe, ya ce, “Makiyaya sun kashe wani a safiyar yau (Talata) a kauyen Tsenge, sannan kuma an kashe wasu mutane hudu a unguwar Babowa ranar Lahadi.”

punch newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp