fidelitybank

An haramta wa manyan motocin dakon man fetur hawa tituna a Najeriya

Date:

Hukumar kula da harkokin sarrafawa da tacewa da sufurin man fetur a Najeriya, NMDPRA ta bayyana haramta wa tankokin dakon man fetur ɗaukar lita 60,000 daga ranar 1 ga watan Maris mai zuwa domin rage yawaitar haɗurran tankokin dakon man mai a kan titunan ƙasar.

Babban daraktar hukumar, mai lura rarrabawa da wuraren adana man, Ogbugo Ukoha ne ya bayyana hakan lokacin da yake zantawa da menama labarai bayan taron masu ruwa da tsaki na hukumar.

Ya ce ɗaukar matakin ya zama wajibi la’akari da ƙaruwar haduran tankokin mai a kan titunan ƙasar, da a wasu lokuta ke zuwa mummunar asarar rayuka.

Ya ce taron masu ruwa da tsakin – wanda ya samu halarta hukumomin tsaro da masu kula da sufuri kamar hukumar DSS da ta hukumar kiyaye aukuwar hadura da ƙungiyoyin NARTO da NUPENG da SON da DAPPMAN da MEMAN da NMDPRA – ya ɗauki matakin cewa ba za a bar duk tankar da ke ɗauke da litar mai fiye da 60,000 ta hau kan titi ba.

A baya- bayan nan dai hatsuran tankokin man fetur a ƙasar ya haifar da asarar rayuka masu yawa.

today nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp