fidelitybank

An haramta nuna fim mai fadan Daba da harkar Daudu a Kano

Date:

Hukumar tace fina-finai ta jihar Kano, ta sanar da matakin haramta shirya fina-finan da ke nuna faɗan daba da harkar Daudu.

Shugaban hukumar, Abba El-Mustapha ne ya sanar da matakin ranar Laraba bayan ganawa da manyan ma’aikatan hukumar tace fina-finai na jihar da wasu wakilai daga masana’antar shirya fina-finai ta Kannywood.

Bayanin na ƙunshe cikin sanarwar da jami’in yaɗa labarai na hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman ya sanyawa hannu.

El-Mustapha ya bayyana cewa, hukumar tana da sahhalewar doka ta dakatar da duk wani fim da take ganin zai ci karo da tarbiyya da al’adar al’ummar jihar Kano.

Shugaban hukumar ya kuma bai wa masu shirya fina-finai nan da wata ɗaya da su gyara ayyukansu kafin dokar ta soma aiki.

Ya kuma ce, “Lokaci ya wuce da za a naɗe hannu kan fina-finan da ke gurɓata tarbiyyar al’umma”. In ji Abba.

sun newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp