Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal, ya haramta dukkan ayyukan hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba a faɗin jihar, inda ya buƙaci jami’an tsaro su ɗauki tsauraran matakai kan waɗanda suka yi biris da umarnin.
Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya fitar a ranar Asabar, ta ce gwamnatin jihar ta lura cewa aikin hakar ma’adinan ba bisa ka’ida ba ya taka rawa wajen ƙaruwar ayyukan ƴan bindiga a jihar.
Gwamna Dauda ya ce lokaci ya yi da za a kawo karshen hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba da kuma ɗaukar matakai da za su kare lafiyar mutane.
“Na bai wa jami’an tsaro umarnin harbi kan duk wanda aka samu yana hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba.
“Mun ɗauki matakin ne don tabbatar da lafiyar al’ummar Zamfara da kuma jan kunnen masu aikata irin wannan laifi,” in ji gwamnan.
Dauda ya kuma ce sun ɗauki matakin ne domin ganin albarkatun jihar sun dawo karkashin ikon gwamnati