fidelitybank

An haramta haƙar ma’adanai a Zamfara

Date:

Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal, ya haramta dukkan ayyukan hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba a faɗin jihar, inda ya buƙaci jami’an tsaro su ɗauki tsauraran matakai kan waɗanda suka yi biris da umarnin.

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya fitar a ranar Asabar, ta ce gwamnatin jihar ta lura cewa aikin hakar ma’adinan ba bisa ka’ida ba ya taka rawa wajen ƙaruwar ayyukan ƴan bindiga a jihar.

Gwamna Dauda ya ce lokaci ya yi da za a kawo karshen hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba da kuma ɗaukar matakai da za su kare lafiyar mutane.

“Na bai wa jami’an tsaro umarnin harbi kan duk wanda aka samu yana hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba.

“Mun ɗauki matakin ne don tabbatar da lafiyar al’ummar Zamfara da kuma jan kunnen masu aikata irin wannan laifi,” in ji gwamnan.

Dauda ya kuma ce sun ɗauki matakin ne domin ganin albarkatun jihar sun dawo karkashin ikon gwamnati

legit news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp