Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya umarci jami’an tsaro da su kama ƴandaba da duk waɗanda ke da hannu wajen tayar da zaune tsaye a Minna, babban birnin jihar.
Bago ya bayar da umarnin ne bayan samun tashe-tashen hankula a birnin na Minna.
Umarnin nasa ya hada da kama mutanen da ke yawo da gashin dada.
Tuni dai gwamnatin jihar ta sanya dokar takaita zirga-zirgar mutane da baburan haya, domin magance rikicin ƴandaba da birnin ke fama da shi.
Lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar akalla mutane goma, kamar yadda rahotanni suka bayyana.