fidelitybank

An haramta amfani da TikTok a Somaliya

Date:

Somaliya ta dakatar da kafofin dandalin sada zumunta na TikTok da Telegram, tare da shafin caca na 1XBet.

Dalilin da ya sa gwamnatin kasar ta dauki wannan mataki shi ne ikirarin cewa “kungiyoyin ‘yan ta’adda da kungiyoyin da ke da hannu wajen yada abubuwan da ba su dace ba” suna amfani da wadannan kafafen yada labarai ne wajen yaudarar jama’a.

Wannan ya zo ne daidai lokacin da Somaliyya ta bayyana kudurinta na fatattakar mayaƙan al-Shabab, wadanda ke ci gaba da rike madafun iko a wasu sassa na kasar da kuma burin cimma wannan gagarumin buri a cikin watanni biyar masu zuwa.

Ma’aikatar sadarwa da fasaha ta Æ™asar ta umarci kamfanoni masu samar da intanet da su aiwatar da dokar kafin ranar 24 ga watan Agusta inda suka ce rashin yin biyayya zai iya haifar da matakin shari’a da ba a fayyace ba.

A yayin wani taro na baya-bayan nan kan harkokin tsaro na intanet da na sada zumunta da aka gudanar a birnin Mogadishu, babban birnin kasar, an yi nuni da irin illar da shafukan intanet ke yi wa matasa kuma sun taimaka wajen asarar rayuka.

legit news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka Æ´an Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar HaÉ—in kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran Æ™asa za ka mayar da kai ba zaÉ“en 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp