fidelitybank

An hana zirga-zirga a Filato sakamakon rikici

Date:

Hukumomi a jihar Filato sun sanar da sanya dokar hana zirga-zirga a yankin Bwai na ƙaramar hukumar Mangu.

Wata sanarwa da ta samu sa hannun shugaban ƙaramar hukumar Mangu, Minista Daput, ta ce an amince da sanya dokar ne domin dawo da zaman lafiya, bayan wani hari da aka kai wanda ya yi sanadin rayukan kimanin mutum 20.

Bayanai sun nuna cewa wasu mahara ne suka far wa ƙauyukan da asubahin ranar Talata inda suka cinna wa gidaje wuta.

Haka nan maharan sun riƙa far wa al’umma da ke ƙoƙarin tserewa, wanda hakan ya haifar da mutuwar mutane da dama da kuma raunata wasu.

Ya zuwa yanzu an gano gawarwaki kimanin 20 a ƙauyukan Fungzai da Kubat.

Bayanan sun ƙara da cewa ana ci gaba da bincike domin gano ko akwai sauran waɗanda suka mutu ko suka raunata a sanadiyyar harin.

Mai magana da yawun rundunar ƴan sanda a jihar ta Filato, DSP Alfred Alabo ya ce sun tura da ƙarin jami’ansu domin tabbatar da zaman lafiya da gudanar da bincike.

daily post news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp