Rundunar Sojin Kamaru ta tabbatar da kisan sojojinta 12 a garin Wulgo a arewa maso gabashin Najeriya, sakamakon wani hari da masu iƙirarin jihadi suka kai musu, da ya bar wasu da raunuka.
Wata Sanarwa da mai magana da yawun rundunar sojin ta Kamaru Cyrille Serge Atonfack ya fitar, ya ce masu iƙirarin jihadin a baya-bayan nan sun kutsa ɗaya daga cikin wuraren rundunar haɗin guwiwar ƙasa da ƙasa da ke kusa da garin Fotokol mai iyaka da Kamaru, nan ma suka kai hari kan dakarun.
An aike da gawarwaki ga iyalan su, wasu kuwa suna ɗakin ajiyar gawarwaki, yayin da waɗanda suka sami raunuka an aike da su asibiti a Chadi.
Rundunar sojin ta kuma ce an hallaka masu iƙirarin jihadi da dama, sai dai bata bayar da adadin su ba ko kuma ƴan wani ɓangare ne.
Tsawon shekaru yankin tafkin Chadi na fama da hare-hare da kisan mutane da ake zargin yan ƙungiyar boko haram da mayaƙan ISWAP ne keyi, sai dai duk da irin ƙokarin da dakarun haɗin gwiwa na ƙasashen Najeriya da Kamaru da Chadi da Nijar ke yi, har yanzu masu iƙirarin jihadin na ci gaba da gudanar da ayyukansu a yankin.