fidelitybank

An hallaka Sojojin Kamaru a iyakar Najeriya

Date:

Rundunar Sojin Kamaru ta tabbatar da kisan sojojinta 12 a garin Wulgo a arewa maso gabashin Najeriya, sakamakon wani hari da masu iƙirarin jihadi suka kai musu, da ya bar wasu da raunuka.

Wata Sanarwa da mai magana da yawun rundunar sojin ta Kamaru Cyrille Serge Atonfack ya fitar, ya ce masu iƙirarin jihadin a baya-bayan nan sun kutsa ɗaya daga cikin wuraren rundunar haɗin guwiwar ƙasa da ƙasa da ke kusa da garin Fotokol mai iyaka da Kamaru, nan ma suka kai hari kan dakarun.

An aike da gawarwaki ga iyalan su, wasu kuwa suna ɗakin ajiyar gawarwaki, yayin da waɗanda suka sami raunuka an aike da su asibiti a Chadi.

Rundunar sojin ta kuma ce an hallaka masu iƙirarin jihadi da dama, sai dai bata bayar da adadin su ba ko kuma ƴan wani ɓangare ne.

Tsawon shekaru yankin tafkin Chadi na fama da hare-hare da kisan mutane da ake zargin yan ƙungiyar boko haram da mayaƙan ISWAP ne keyi, sai dai duk da irin ƙokarin da dakarun haɗin gwiwa na ƙasashen Najeriya da Kamaru da Chadi da Nijar ke yi, har yanzu masu iƙirarin jihadin na ci gaba da gudanar da ayyukansu a yankin.

assu today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp