fidelitybank

An hallaka Sojojin Kamaru a iyakar Najeriya

Date:

Rundunar Sojin Kamaru ta tabbatar da kisan sojojinta 12 a garin Wulgo a arewa maso gabashin Najeriya, sakamakon wani hari da masu iƙirarin jihadi suka kai musu, da ya bar wasu da raunuka.

Wata Sanarwa da mai magana da yawun rundunar sojin ta Kamaru Cyrille Serge Atonfack ya fitar, ya ce masu iƙirarin jihadin a baya-bayan nan sun kutsa ɗaya daga cikin wuraren rundunar haɗin guwiwar ƙasa da ƙasa da ke kusa da garin Fotokol mai iyaka da Kamaru, nan ma suka kai hari kan dakarun.

An aike da gawarwaki ga iyalan su, wasu kuwa suna ɗakin ajiyar gawarwaki, yayin da waɗanda suka sami raunuka an aike da su asibiti a Chadi.

Rundunar sojin ta kuma ce an hallaka masu iƙirarin jihadi da dama, sai dai bata bayar da adadin su ba ko kuma ƴan wani ɓangare ne.

Tsawon shekaru yankin tafkin Chadi na fama da hare-hare da kisan mutane da ake zargin yan ƙungiyar boko haram da mayaƙan ISWAP ne keyi, sai dai duk da irin ƙokarin da dakarun haɗin gwiwa na ƙasashen Najeriya da Kamaru da Chadi da Nijar ke yi, har yanzu masu iƙirarin jihadin na ci gaba da gudanar da ayyukansu a yankin.

tribune newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp