fidelitybank

An gurfnara da mutanen da ake zargi da satar tukunyar iskar gas

Date:

Rundunar ‘yan sanda a Legas ta gurfanar da wasu mutane biyu, Ifeanyi Chukwu da Amadi Orji a gaban wata kotun Majistare ta Ojo da ke Legas, bisa zargin su da satar tukunyar iskar gas.

Chukwu, mai shekaru 42 da Orji, mai shekaru 50, suna gurfana a gaban kotun Majistare, Mista LK J Layeni, bisa tuhume-tuhume biyu da suka shafi hada baki da sata.

Sai dai sun musanta zargin da ake musu.

Tun da farko dai mai gabatar da kara, Dokta Simon Uche ya shaida wa kotun cewa wadanda ake tuhumar sun aikata laifin ne a watan Disambar 2022, a sashen Fancy and Furniture na kasuwar kasa da kasa ta Alaba da ke Ojo, Legas.

Ya kara da cewa wadanda ake tuhumar sun hada baki ne wajen satar iskar gas mallakin wani Victor Nzekwe, inda ya kara da cewa kudin silinda din ya kai Naira miliyan 20.

A cewarsa, daga karshe ‘yan sanda sun cafke wadanda ake tuhuma tare da gurfanar da su a gaban kotu.

Laifin a cewarsa ya sabawa tanadin sashe na 287 da na 411 na dokar laifuka ta jihar Legas 2015.

Don haka Alkalin kotun ya bayar da belin wadanda ake tuhumar a kan kudi Naira miliyan daya kowanne tare da masu tsaya masa guda biyu kowannensu a daidai wannan adadi sannan ya dage ci gaba da sauraron karar har zuwa ranar 7 ga watan Fabrairun 2024 domin ambato.

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp