fidelitybank

An gurfanar da wata mata a kotu saboda ta saka danta karami a matsayin soja

Date:

Wata kotu a kasar Sweden ta tuhumi wata mata ‘yar kasar  da aikata laifukan yaki saboda ta taimaka wajen sanya danta mai shekaru 12 a matsayin sojan a kasar Syria, inda a ka kashe shi a yakin basasar da su ke tafkawa.

Kamfanin dilancin labarai na Reuters ya rawaito cewa, matar mai shekaru 49, ‘yar kasar Sweden da ta dawo daga kasar Syria a shekarar 2020, ita ce mutum ta farko da a ka sani da a ka tuhume ta a Sweden da laifin taimakawa daukar karamin danta a matsayin soja.

Yaron, wanda a ka haifa a shekara ta 2001, ya fara gwagwarmaya ne tun a shekara ta 2013, domin shiga kungiyoyin da su ka hada da na IS. Ya kuma mutu a cikin shekarar 2017, sai dai hukumomi ba su fitar da wani karin bayani game da mahaifiyar ko ɗanta ba.

A zaman kotu na ranar Talatar nan, matar ta musanta zargin, ta hannun lauyanta, Mikael Westerlund.

Sai dai kotun ta ce har Idan a ka same ta da laifi za ta fuskanci hukuncin daurin shekaru hudu a gidan yari, inji mai gabatar da kara Reena Devgun.

A cewar Majalisar Dinkin Duniya, daukar yara ‘yan kasa da shekaru 15 aiki da kuma amfani da su a matsayin sojoji haramun ne a karkashin dokar jin kai ta kasa da kasa, kuma kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa ta amince da shi a matsayin laifin yaki.

A karkashin dokar Sweden, kotuna na iya yi wa mutane shari’a da laifukan da su ka saba wa dokokin kasa da kasa da a ka aikata a kasashen waje. Za kuma a ci gaba da shari’ar ne a ranar Litinin 10 ga watan Janairu.

the nation news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...
X whatsapp