Kotun shari’ar musulunci a yankin Birgade a Kano karkashin mai shari’a, Isa Rabiu Gaya, an gurfanar da wani mutum, Abdulkuddus Akilu, bisa tuhumarsa da zamba cikin aminci.
Mai gabatar da kara Ditective Aliyu Abidin shi ne ya karanto masa kunshin tuhumar, amma ya musanta laifin.
A na zargin mutumin da karbar kudi Naira miliyan shida a hannun wanda yai karar, Mustapha Lawan Gogari a matsayin zai ba shi dalar Amurka, amma daga bisani babu Naira kuma babu Dalar, hakan ya sanya a ka gurfanar dashi a gaban kotu.
Sai dai kotun ta kara tsayar da shi a hannun beli, sannan wanda zai tsaya masa har idan yagudu zai biya kudin da ya karba Naira miliyan shida, za kuma a ci gaba da shari’ar a ranar 14 ga watannan domin ci gaba da sauraran shari’ar.