Rundunar ‘yan sanda a jihar Enugu, ta kama wata mata tare da gurfanar da ita a gaban kotu, bisa zarginta da karbar kudi kafin ta bai wa masu su katin zabe.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Daniel Ndukwe, ya tabbatar da hakan a ranar Alhamis.
Ndukwe ya ce an bayar da belin wanda ake zargin tare da wanda ake zargin kuma aka dage sauraron karar zuwa ranar 15 ga watan Fabrairu domin ci gaba da sauraren karar.
Karanta Wannan: Emefiele ya garzaya wajen Buhari bayan umarnin kotu
“Jami’an ‘yan sanda da ke aiki a sashin binciken manyan laifuka na jihar Enugu a ranar 31 ga watan Janairu, 2023, sun kama wata mata da ake zargi, Chinwendu Nnamani, mai shekaru 41.
“Nnamani na da hannu a cikin wani faifan bidiyo na kafafen sada zumunta wanda aka gan ta ana zarginta da sayar da katunan zabe na dindindin (PVCs) na INEC akan kudi Naira Dubu daya a wata makarantar firamare da ke Emene, Enugu.
“Haka kuma an kama wani Nkiruka Patience Obinna, mai shekaru 38, wadda aka bayyana a matsayin ma’aikaciyar INEC, kuma ana zarginta da bayar da irin wadannan PVCs ga wanda ake zargi na farko don rabawa ga ainihin masu su.
“An kammala bincike, an gurfanar da karar a gaban kotu bisa tanadin dokar zabe ta 2022, kuma an gurfanar da wadanda ake zargin,” in ji shi.