An gurfanar da wata mai karbar kudi a kotun shari’ar Musulunci ta Jihar Kano, Hussaina Imam da wasu mutum 14 da suka hada da alkalai da masu rijista a gaban wata kotun majistare da ke jihar bisa zargin karkatar da zunzurutun kudi har Naira miliyan 500 da aka ware wa marayu.
A lokacin gudanar da shari’ar ranar Laraba a gaban Alkalin Kotun Mai shari’a Mustapha Sa’ad Datti, an zargi wadanda ake tuhumar da aikata laifin da ya shafi hada baki da cin amana da ma’aikatan gwamnati da kuma sata.
Mai shari’an ya ce laifin ya saɓawa sashe na 97 da 79 da 315 da 289 na kundin Penal Code.
Rahoton farko da aka fitar, ya nuna cewa wadanda ake zargin, Bashir Ali Kurawa da Saadatu Umar da Tijjani Abdullahi da Maryam Jibrin Garba da Shamsu Sani da kuma Hussaina Imam, sun aikata laifi a shekarar 2020/2021, inda Imam ta yi amfani da mukaminta na mai karɓar kudi a kotun daukaka kara ta shari’ar musulunci ta jihar Kano wajen hada baki da wasu.
Ana zargin ta da laifin buga jabun wasikun kotun Shari’a tare da sace kudi har naira miliyan ɗari hudu da tamanin da takwas da ‘yan kai mallakin kotun daukaka karar shari’ar Musulunci ta jihar Kano.
Sai dai duk waɗanda ake zargi sun musanta aikata laifin da ake tuhumar su da shi, inda lauyan da ke kare su ya bukaci kotu ta bayar da belin su.