fidelitybank

An gurfanar da mai karbar kudi a kotu da wasu alkalai akan zargin cinye kudin marayu

Date:

An gurfanar da wata mai karbar kudi a kotun shari’ar Musulunci ta Jihar Kano, Hussaina Imam da wasu mutum 14 da suka hada da alkalai da masu rijista a gaban wata kotun majistare da ke jihar bisa zargin karkatar da zunzurutun kudi har Naira miliyan 500 da aka ware wa marayu.

A lokacin gudanar da shari’ar ranar Laraba a gaban Alkalin Kotun Mai shari’a Mustapha Sa’ad Datti, an zargi wadanda ake tuhumar da aikata laifin da ya shafi hada baki da cin amana da ma’aikatan gwamnati da kuma sata.

Mai shari’an ya ce laifin ya saÉ“awa sashe na 97 da 79 da 315 da 289 na kundin Penal Code.

Rahoton farko da aka fitar, ya nuna cewa wadanda ake zargin, Bashir Ali Kurawa da Saadatu Umar da Tijjani Abdullahi da Maryam Jibrin Garba da Shamsu Sani da kuma Hussaina Imam, sun aikata laifi a shekarar 2020/2021, inda Imam ta yi amfani da mukaminta na mai karÉ“ar kudi a kotun daukaka kara ta shari’ar musulunci ta jihar Kano wajen hada baki da wasu.

Ana zargin ta da laifin buga jabun wasikun kotun Shari’a tare da sace kudi har naira miliyan É—ari hudu da tamanin da takwas da ‘yan kai mallakin kotun daukaka karar shari’ar Musulunci ta jihar Kano.

Sai dai duk waÉ—anda ake zargi sun musanta aikata laifin da ake tuhumar su da shi, inda lauyan da ke kare su ya bukaci kotu ta bayar da belin su.

guardian newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...

Mukarraban gwamnati ba zan lamunci dabi’ar zubar da kima ta ba – Abba

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya gargaÉ—i masu...

WAEC ta sake bude shafinta don duba jarabawar bana

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma (WAEC) ta bayyana...

Indonesia za ta gina asibiti dubu biyu ga FalasÉ—inawa

Indonesia ta sanar da cewa za ta kafa wata...

Lauyan Sowore ya bukaci a sake shi cikin gaggawa

Lauyoyin ffitaccen É—an gwagwarmayar nan kuma É—an jarida, Omoyele...

Najeriya da Indiya za su haɗa kai na yaƙi da fataucin miyagun ƙwayoyi

Hukumar hana sha da fatauncin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya,...

Jihohi 19 da za a yi kwana 9 a na ruwan sama harda Kano – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen za a shafe kwana...

Tinubu ya mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar matar MKO Abiola

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa bisa...

Abubuwan da Kwamiti ya gano a wajen Kwamishina mai murabus na Kano

A ranar Litinin ne kwamitin binciken badaƙalar belin Danwawu,...
X whatsapp