fidelitybank

An gurfanar da mai karbar kudi a kotu da wasu alkalai akan zargin cinye kudin marayu

Date:

An gurfanar da wata mai karbar kudi a kotun shari’ar Musulunci ta Jihar Kano, Hussaina Imam da wasu mutum 14 da suka hada da alkalai da masu rijista a gaban wata kotun majistare da ke jihar bisa zargin karkatar da zunzurutun kudi har Naira miliyan 500 da aka ware wa marayu.

A lokacin gudanar da shari’ar ranar Laraba a gaban Alkalin Kotun Mai shari’a Mustapha Sa’ad Datti, an zargi wadanda ake tuhumar da aikata laifin da ya shafi hada baki da cin amana da ma’aikatan gwamnati da kuma sata.

Mai shari’an ya ce laifin ya saɓawa sashe na 97 da 79 da 315 da 289 na kundin Penal Code.

Rahoton farko da aka fitar, ya nuna cewa wadanda ake zargin, Bashir Ali Kurawa da Saadatu Umar da Tijjani Abdullahi da Maryam Jibrin Garba da Shamsu Sani da kuma Hussaina Imam, sun aikata laifi a shekarar 2020/2021, inda Imam ta yi amfani da mukaminta na mai karɓar kudi a kotun daukaka kara ta shari’ar musulunci ta jihar Kano wajen hada baki da wasu.

Ana zargin ta da laifin buga jabun wasikun kotun Shari’a tare da sace kudi har naira miliyan ɗari hudu da tamanin da takwas da ‘yan kai mallakin kotun daukaka karar shari’ar Musulunci ta jihar Kano.

Sai dai duk waɗanda ake zargi sun musanta aikata laifin da ake tuhumar su da shi, inda lauyan da ke kare su ya bukaci kotu ta bayar da belin su.

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp