fidelitybank

An gudanar da addu’o’in samun sauƙin rayuwa a Kano

Date:

Duk da kiraye-kirayen da aka rinƙa yi na neman a ɗage addu’o’i na musamman da aka tsara za a fara yi daga yau Asabar a Najeriya, bayanai sun nuna cewa an gudanar da addu’ar a masallacin, gidan Isiyaku Rabi’u da ke Goron Dutse, a yankin, ƙaramar hukumar Dala, da ke Kano.

Jaridar daily Trust ta ruwaito cewa, wani mai amfani da shafukan sada zumunta da muhawara ya sanya a shafinsa na Facebook cewa: ”Ana karatun Qur’ani daga nan masallacin Khalifa Isyaku Rabiu, Goron Dutse, Kano, domin addu’a kan halin da kasarmu ke ciki, Allah Ya sawƙaƙa mana, Amin.”

Daman jaridar ta ruwaito cewa, ɗaya daga cikin mutanen da suka shirya addu’ar ƙasa da za a fara yau Asabar 10 ga watan Agusta, 2024, a masallacin na Isiyaku Rabi’u, da kuma sauran jihohin ƙasar, Mubarak Ibrahim Lawan, ya sanar da cewa an fasa saboda dalilai na tsaro, ganin yadda zanga-zangar lumana da aka fara a ranar 1 ga watan nan na Agusta ta tsawon kwana goma ta rikiɗe a wasu jihohin ta zama tarzoma, inda aka rinka sace-sace da ɓarnata dukiya ta gwamnati ta ‘yan kasuwa da sauransu, har ma da kisa da raunata jama’a, wanna ya sa wasu suka yi, tunanin karkata ga addu’a domin samun sauƙi a kan matsalolin da ke addabar ƙasar.

A wani saƙo na bidiyo da ya fitar, a Kano, Mubarak, ya ce, kwamishinan ƴansanda na jihar, da kuma darektan hukumar tsaro ta DSS shi ma na jihar sun ankarar da su cewa wasu ɓata-gari a ƙasar sun shirya tura wasu miyagu wajen taron addu’ar, domin cimma manufarsu.

Ya ce, an yi zargin cewa za su jagoranci wasu matasa da za su riƙa kwashe kayan jama’a da na hukuma, da sace-sace, kamar yadda aka yi a baya a lokacin da aka fara zanga-zanga, a saboda haka ya ce sun fasa taron addu’o’in.

thisday newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp