Gwamnatin Najeriya ta sanar da wasu sabbin dokokin da suka shafi samar da takardun izinin shiga ƙasar ga ƴanƙasashen waje, inda ta yi gargaɗin cewa masu karya doka za su iya fuskantar haramcin sake samun damar shiga Najeriyar har na tsawon shekara 10.
Wannan matakin dai zai soma aiki nan da watan gobe na Mayu.
A cewar ministan harkokin cikin gida na Najeriya, Olubunmi Tunji-Ojo, za a tabbatar da an tantance waɗanda za su shiga ƙasar, tare da cin waɗanda bizarsu ta ƙare amma ba su sabunta ba tarar dala 15 kowace rana.