Rundunar sojin Najeriya ta gargadi jamiāanta kan duk wani abu da ya sabawa doka a lokacin zabe mai zuwa.
Darektan Jarrabawa, Sashen Kula da Ma’aunin Sojoji (DASE), Birgediya Janar Adamu Yari Yakubu ne ya yi wannan gargadin a wata ziyara da ya kai wa dakarun da ke gadin Brigade.
Janar din da tawagarsa sun kasance a sansanin āyan gudun hijira na Brigade Forward Operations Base da ke karamar hukumar Kwali a babban birnin tarayya (FCT).
Karanta Wannan:Ā Sojoji sun kashe ‘yan bindiga a Zamfara
Yakubu ya umurci sojojin da su tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali ga duk masu kada kuriāa, a cewar Kyaftin Geoffrey Abakpa, jamiāin hulda da jamaāa Brigade.
Ya yaba da matakin da dakarun hadin gwiwa suka yi na shirye-shiryen, ya kara da cewa “hadin kai shine mabuÉin don tabbatar da samun sahihin zaÉe”
Yakubu ya kuma shawarci āyan Najeriya da su rika gudanar da rayuwarsu ta hanyar da ta dace, yana mai jaddada cewa ba za a amince da tashe-tashen hankulan zabe ba.
Kwamandan Guards Brigade, Birgediya Janar Aminu Umar ya samu wakilcin mataimakin babban hafsan soji, Laftanar Kanar Kayode Akinsowon.
Aminu ya bada tabbacin cewa rundunar na aiki da jamiāan tsaro domin tabbatar da zaman lafiya a Abuja kafin zabe da kuma bayan zabe.
Ya kara da cewa, an wayar da kan rundunonin hadin gwiwar sojojin kan dokokin zabe da kuma kaāidojin aiki na rundunar sojin kasar.