fidelitybank

An gargadi Borno da Yobe da Jigawa su zama cikin shirin ambaliya

Date:

Akwai yiwuwar samun ambaliya a jihohin Borno, Jigawa da Yobe, kamar yadda Hukumar Yanayi ta Najeriya (NiMet) ta sanar a wani hasashen yanayi da ta fitar a shafinta na X.

Hukumar ta ce tsawa da ruwan sama matsakaici na iya sauka a wasu sassan arewacin Najeriya wadda zai iya haddasa ambaliyar ruwan.

NiMet ta bayyana cewa da safiyar yau Talata, ana sa ran ruwan sama a jihohin Borno, Yobe, Jigawa, Gombe, Bauchi, Adamawa, Kaduna da Taraba.

Hakanan, da yamma zuwa dare, ana sa ran yawancin jihohin Arewa za su ci gaba da samun ruwan sama tare da iska da tsawa.

A tsakiyar Najeriya kuwa, hasashen ya nuna cewa za a samu yanayin giragizai da safe, sannan da yamma za a samu ruwan sama matsakaici a wasu sassan Nasarawa, Benue, Kogi, Kwara, Neja, Filato da kuma babban birnin tarayya Abuja.

NiMet ta kuma bayyana cewa a Kudancin Najeriya, da safe ana sa ran yanayi mai giragizai tare da yiwuwar ruwan sama a wurare kaÉ—an, yayin da a Yammaci ake hasashen ruwan sama a lokuta daban-daban.

Hukumar ta yi gargaɗi ga al’ummar da ke zaune a wuraren da ke da haɗarin fuskantar ambaliya da su ɗauki matakan kariya. Ta kuma shawarci hukumomin agaji da sauran masu ruwa da tsaki da su kasance cikin shiri domin bada taimako idan buƙata ta taso.

www.leadership ng.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp