fidelitybank

An gargadi Alhazan Najeriya kar su sayarwa da Takarai tufafin da aka basu

Date:

Hukumar alhazan kasa, NAHCON ta gargadi maniyyatan kasar kan sayar wa wadanda ke zaune a Saudiyya domin neman kudi da aka fi sani da ‘takari’ tufafin da hukumar ta dinka musu domin gudanar da ayyukan hajjin.

Daraktan Da’awah na hukumar ta NAHCON reshen jihar Kebbi, Sheikh Aminu Hassan ne ya bayyana haka lokacin da yake yi wa maniyyatan jhar jawabi bayan isarsu kasa mai tsarki.

Akwai zarge-zargen cewa takarin na sayen tufafin wasu maniyyatan musamman mata da kudi masu yawan gaske, tare da yin bad da bami domin shiga cikinsu da fakewa da aikin hajjin wajen aikata abubuwan da ba su dace ba.

Sheikh Aminu Hassan ya ce sayar da tufafin babban laifi ne da zai iya janyo wa duk wanda ya aikata hukunci mai tsanani, don haka ne ya gargadi maniyyatan su kauce wa wannan mummunar dabi’a.

“Hakika za ka iya samun kudi masu yawa a wajen takarin, musamman ku mata, to amma ku tuna cewa za su yi amfani da tufafin ne wajen aikata barna, sannan ku sani cewa za a danganta barnar da Najeriya da ma jihar Kebbi musamman”, in ji shi.

Daraktan ya kara da cewa ”ku tuna cewa tufafinku alama ce ta kasa da jihar da kuka fito, don haka ku kiyaye duk wani abu da zai bata wa kasarku suna”.

Sheikh Aminu Hassan ya kuma yi kira ga maniyyatan su kauce wa yawan kashe kudade babu gaira babu dalili sannan su lura sosai wajen yin canji domin kauce wa fadawa hannun mazambata lokacin gudanar da aikin hajin na bana.

Hukumar alhazan Najeriya, NAHCON ta gargadi maniyyatan kasar kan sayar wa wadanda ke zaune a Saudiyya domin neman kudi da aka fi sani da ‘takari’ tufafin da hukumar ta dinka musu domin gudanar da ayyukan hajjin.

Daraktan Da’awah na hukumar ta NAHCON reshen jihar Kebbi, Sheikh Aminu Hassan ne ya bayyana haka lokacin da yake yi wa maniyyatan jhar jawabi bayan isarsu kasa mai tsarki.

Akwai zarge-zargen cewa takarin na sayen tufafin wasu maniyyatan musamman mata da kudi masu yawan gaske, tare da yin bad da bami domin shiga cikinsu da fakewa da aikin hajjin wajen aikata abubuwan da ba su dace ba.

Sheikh Aminu Hassan ya ce sayar da tufafin babban laifi ne da zai iya janyo wa duk wanda ya aikata hukunci mai tsanani, don haka ne ya gargadi maniyyatan su kauce wa wannan mummunar dabi’a.

“Hakika za ka iya samun kudi masu yawa a wajen takarin, musamman ku mata, to amma ku tuna cewa za su yi amfani da tufafin ne wajen aikata barna, sannan ku sani cewa za a danganta barnar da Najeriya da ma jihar Kebbi musamman”, in ji shi.

Daraktan ya kara da cewa ”ku tuna cewa tufafinku alama ce ta kasa da jihar da kuka fito, don haka ku kiyaye duk wani abu da zai bata wa kasarku suna”.

Sheikh Aminu Hassan ya kuma yi kira ga maniyyatan su kauce wa yawan kashe kudade babu gaira babu dalili sannan su lura sosai wajen yin canji domin kauce wa fadawa hannun mazambata lokacin gudanar da aikin hajin na bana.

legit.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp