fidelitybank

An gargaɗi Tinubu a kan tura Sojoji zuwa jamhuriyar Nijar

Date:

Babban Lauyan Najeriya, SAN, Jibrin Samuel Okutepa, ya gargadi shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, a kan tura sojojin Najeriya domin warware rikicin jamhuriyar Nijar.

A ranar Juma’ar da ta gabata ne Tinubu ya aike da wasika zuwa ga majalisar dattawan Najeriya, inda ya nemi amincewar daukar matakin soji da sauran takunkumi kan jami’an sojin da suka kwace mulki a Nijar.

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio ne ya karanta wasikar a zauren Majalisar.

Sai dai Okutepa, a wasu jerin sakonnin da ya wallafa a shafinsa na Twitter a safiyar ranar Asabar, ya yi fatan majalisar dokokin kasar ba za ta amince da bukatar Tinubu na tura sojojin Najeriya zuwa Nijar domin yakar ‘yakin da ba shi da ma’ana’ na maido da mulkin dimokradiyya a kasar.

Ya wallafa a shafinsa na Twitter cewa, “Ina fata kawai majalisar dokokin kasar ba za ta amince da bukatar tura sojojinmu zuwa jamhuriyar Nijar domin yaki da rashin imani na maido da mulkin dimokradiyya a kasar ba.

“Yan Najeriya na bukatar hukumomin tsaron mu da suka hada da sojoji domin dawo da zaman lafiya da tsaro a Najeriya.”

A halin da ake ciki dai gwamnatin mulkin sojan Nijar ta katse huldar diflomasiyya da Najeriya bayan da wakilin ECOWAS da ta aika zuwa kasar domin samar da zaman lafiya ya kasa cimma wani sakamako.

A watan da ya gabata ne dai gwamnatin mulkin soji ta hambarar da zababben shugaban Jamhuriyar Nijar, Mohamed Bazoum.

nnn news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp