Rundunar ƴansanda ta jihar Kogi ta nemi da Sanata Natasha Akpoti ta soke shirinta na yin gangamin bikin Sallah a mazaɓarta ta Kogi ta tsakiya.
A wata sanarwa da rundunar ta fitar ranar Talata, mai ɗauke da sa-hannun kakakin ƴansandan na jihar, ASP William Aya, kwamishinan ƴansandan jihar, William Ɗantawaye ya ce gangamin ya ci karo da haramcin gudanar da gangamin siyasa da gwamnatin jihar ta yi ranar Litinin.
“Kiran a soke gangamin ya zama dole ne bisa rahotannin sirri da muka samu dangane da ƙoƙarin wasu ɓata gari na yin karkatar da gangamin zuwa wani abu daban da ka iya jefa jihar cikin tashin hankali. Kuma rundunar ƴansandan ba za ta zura ido ta bar duk wani abun da zai jefa jihar mai zaman lafiya zuwa tashin hankali ba.” In ji sanarwar.
A watan da ya gabata ne dai zauren majalisar dattawan Najeriya ya dakatar da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan bisa zargin rashin da’a, bayan ta zargi shugaban majalisar, Godswill Akpabio da cin zarafi da neman ta da lalata.
A baya-bayan nan ne kuma wasu jama’ar da aka ce daga mazaɓarta ne suka aike da ƙorafi zuwa hukumar zaɓe inda suke son yi mata kiranye.
To sai dai magoya bayanta sun shirya gangamin nuna goyon baya a jihar ta Kogi,