fidelitybank

An gargaɗi Tinubu a kan tura Sojoji zuwa jamhuriyar Nijar

Date:

Babban Lauyan Najeriya, SAN, Jibrin Samuel Okutepa, ya gargadi shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, a kan tura sojojin Najeriya domin warware rikicin jamhuriyar Nijar.

A ranar Juma’ar da ta gabata ne Tinubu ya aike da wasika zuwa ga majalisar dattawan Najeriya, inda ya nemi amincewar daukar matakin soji da sauran takunkumi kan jami’an sojin da suka kwace mulki a Nijar.

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio ne ya karanta wasikar a zauren Majalisar.

Sai dai Okutepa, a wasu jerin sakonnin da ya wallafa a shafinsa na Twitter a safiyar ranar Asabar, ya yi fatan majalisar dokokin kasar ba za ta amince da bukatar Tinubu na tura sojojin Najeriya zuwa Nijar domin yakar ‘yakin da ba shi da ma’ana’ na maido da mulkin dimokradiyya a kasar.

Ya wallafa a shafinsa na Twitter cewa, “Ina fata kawai majalisar dokokin kasar ba za ta amince da bukatar tura sojojinmu zuwa jamhuriyar Nijar domin yaki da rashin imani na maido da mulkin dimokradiyya a kasar ba.

“Yan Najeriya na bukatar hukumomin tsaron mu da suka hada da sojoji domin dawo da zaman lafiya da tsaro a Najeriya.”

A halin da ake ciki dai gwamnatin mulkin sojan Nijar ta katse huldar diflomasiyya da Najeriya bayan da wakilin ECOWAS da ta aika zuwa kasar domin samar da zaman lafiya ya kasa cimma wani sakamako.

A watan da ya gabata ne dai gwamnatin mulkin soji ta hambarar da zababben shugaban Jamhuriyar Nijar, Mohamed Bazoum.

latest nigeria newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp