fidelitybank

An gargaɗi ƴan Najeriya mazauna Afrika ta Kudu bayan kammala wasa

Date:

Ofishin jakadancin Najeriya ya shawarci yan kasar da ke zaune a Afirka ta Kudu gabanin wasan da kasashen biyu za su fafata a gasar kwallon Afirka a Ivory Coast.

Sanarwar da ofishin ya fitar ranar Talata ta gargadi yan Najeriya mazauna Afirka ta Kudun su guji tsokanar takwarorinsu idan Super Eagles ta yi nasara a wasan.

Sanarwar ta nemi “yan Najeriya su kula da kalamansu, su kuma yi taka tsan-tsan game da inda za su kalli wasan musamman a wuraren taron jama’a”.

Ta kara da kira ga yan Najeriyar su guji yin murnar wuce gona da iri da ka iya jawo tashin hankali idan har Najeriya ta doke Afirka ta Kudu.

Ofishin jakadancin ya yi gargadi kan mayar da martani ko ta wace fuska a maimakon haka, ofishin ya bukaci mutanen da abin ya shafa su kai korafi kan duk wani yanayi na tashin hankali ga hukumomin da suka dace.

A ranar Juma’ar da ta wuce, kwallon da Ademola Lookman ya zura a ragar Angola ce ta bai wa Super Eagles shiga zagayen kusa da na karshe a gasar ta Afcon.

natforce latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp