fidelitybank

An gano musabbabin hatsarin jirgin saman Indiya

Date:

Masu bincike sun bayyana sakamako na farko-farko game da hatsarin jirgin saman Air India wanda ya yi ajalin mutum 260 cikin watan da ya gabata.

Bayanai da aka samu sun nuna cewa hanyoyin da ke kai mai ga injunan jirgin sun kasance a kashe jim kaÉ—an bayan tashinsa.

Yan dakiku bayan tashin jirgin saman kirar Boeing 787, maballan kunnawa da kashe mai sun kasance a kashe, lamarin da ya hana injinan jirgin samun mai, wanda ya kai ga daukewar lantarki a daukaci jirgin.

Kashe abin da ke kai mai zuwa ga injin jirgi abu ne da ke faruwa bayan saukar jirgin sama, sai dai ganin abin da ya faru, ya bar masu bincike cikin tababa.

A muryar da na’urar jirgin ta nada, an ji daya daga cikin matuka jirgin na tambayar dan’uwansa me ya sa ya kashe man, yayin da shi kuma ya mayar da martani da cewa ” ban kashe ba”.

Daga baya an kunna man, lamarin da ya sanya injinan jirgin suka fara aiki, sai dai a daidai lokacin da jirgin ya fadi kasa daya daga cikin injunan bai kammala dauka ba.

Lamarin dai baki daya ya faru ne a cikin ‘yan dakiku.

Yanzu haka dai masu bincike na ci gaba da nazarin karikitan jirgin da kuma na’urar nadan bayanai domin tantance duk abubuwan da suka faru gabanin hatsarin.

Kwararru a sufurin jiragen sama na kasar Indiya da kuma wasu daga kamfanin Boeing ne ke gudanar da binciken.

Yayin da wasu ke zargin cewa ko akwai yiwuwar wani ne ya yi abin da gangan, kamfanin jirgin saman ya ce matuka jirgin biyu sun tsalake duk wani gwaji da aka yi musu na cancanta kafin shiga jirgin, ciki har da gwajin shan kayan maye.

Sai dai yanzu masu bincike sun karkata ne domin gano ko maballan kunnawa da kashe man jirgin sun ci karo ne da matsala.

nigeria.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp