fidelitybank

An gano gawarwakin ‘yan bindigan da suka tursasa zaman gida a Enugu

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Enugu, ta ce jami’anta sun samu nasarar tarwatsa wani gungun ‘yan bindiga da ke kokarin kakaba dokar zaman gida a jihar.

Cikin wani sako da rundunar ta wallafa a shafinta na Twitter ta ce, a ranar Juma’a da safe ne jami’anta suka gano gawarwakin hudu daga cikin ‘yan bindigar a wani daji da ke garin Awkunanaw, inda suka gudu domin buya.

Sanarwar ta ce dama a ranar Alhamis, jami’a ‘yan sandan suka fatattaki wasu ‘yan bindiga da suka yi yunÆ™urin kwace wata mota daga hannun wani direba, inda maharan suka gudu tare da munanan raunukan harbin bindiga a jikinsu.

Daga nan ne kuma ‘yan sanda suka ce suka fara farautar maharan, inda suka gano makamai masu tarin yawa a lokacin binciken nasu

Kwamishinan ‘yan sandan jihar CP Ahmed Ammani ya tabbatar da cewa jami’an ‘yan sandan jihar da sauran jami’an tsaro ba za su yi kasa a gwiiwa ba har sai sun tabbatar da zaman lafiya da tsaro a fadin jihar, ta yadda mazauna jihar za su rika fita harkokin kasuwancinsu a kowacce rana.

Kungiyar masu tayar da kayar baya ta IPOB dai na tilasta wa mutane zaman gida a wasu ranaku, a wasu yankuna da ke kudu maso gabashin kasar.

nigeria news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp