Sojojin Isra’ila sun gano gawarwakin wasu ‘yan Isra’ila da ƙungiyar Hamas ta yi garkuwa da su lokacin harin da ta kai makon da ya gabata.
Kafofin yaɗa labaran Isra’ila sun ce an gano gawarwakin ne a lokacin wani samame ta ƙasa da sojojin Isra’ila suka kai birnin Gaza ranar Juma’a.
Rahotonni sun ce sojojin Isra’ila sun gano gawarwakin ‘yan ƙasar da ba afayyace adadinsu ba, inda aka mayar da su Isra’ila.
Haka kuma a lokacin samamen an gano wasu kayayyakin mutanen da Hamas din ta yi garkuwa da su.