Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Brazil ta gano dukkan gawarwakin mutanen da jirgin sama ya yi haɗari da su a kusa da birnin São Paulo, a ranar Juma’a.
Dukkan mutum sittin da biyu da ke cikin jirgin sun rasu, daga cikinsu akwai wata tawagar likitoci da ɗaliban jami’a da wasu iyalai uku da ke ƙoƙarin komawa gida daga wata ƙasa.
Bidiyon da aka wallafa a shafukan sada zumunta ya nuna yadda jirgin ya rikito daga sama zuwa ƙasa tare da kamawa da wuta.
Jirgin ya fado ne a wata unguwa da jama’a ke zaune, to amma ba wanda ya ji rauni a wajen da ya fado, sai dai jami’ai sun ce gida daya ya lalace.
Hukumomi sun ce gawarwakin – 34 na maza ne sai kuma 28 mata – kuma an kai su dakin ajiye gawarwaki na ‘yansanda a birnin na São Paulo, inda za a yi kokarin gano su tare da mika su ga iyalansu.
Tuni an riga an gane gawar matukin jirgin da ta mataimakinsa.
Iyalai da ‘yan uwan mutanen za su je domin taimakawa wajen gane gawarwakin.
Ana ci gaba da bincikin dalilin da ya haddasa hadarin.