fidelitybank

An gano gawarwakin mutane 62 da jirgin sama ya hallaka su a Brazil

Date:

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Brazil ta gano dukkan gawarwakin mutanen da jirgin sama ya yi haɗari da su a kusa da birnin São Paulo, a ranar Juma’a.

Dukkan mutum sittin da biyu da ke cikin jirgin sun rasu, daga cikinsu akwai wata tawagar likitoci da ɗaliban jami’a da wasu iyalai uku da ke ƙoƙarin komawa gida daga wata ƙasa.

Bidiyon da aka wallafa a shafukan sada zumunta ya nuna yadda jirgin ya rikito daga sama zuwa ƙasa tare da kamawa da wuta.

Jirgin ya fado ne a wata unguwa da jama’a ke zaune, to amma ba wanda ya ji rauni a wajen da ya fado, sai dai jami’ai sun ce gida daya ya lalace.

Hukumomi sun ce gawarwakin – 34 na maza ne sai kuma 28 mata – kuma an kai su dakin ajiye gawarwaki na ‘yansanda a birnin na São Paulo, inda za a yi kokarin gano su tare da mika su ga iyalansu.

Tuni an riga an gane gawar matukin jirgin da ta mataimakinsa.

Iyalai da ‘yan uwan mutanen za su je domin taimakawa wajen gane gawarwakin.

Ana ci gaba da bincikin dalilin da ya haddasa hadarin.

world news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp