fidelitybank

An gano gawarwakin mutane 1,222 a Ukraine

Date:

Babbar mai shigar da ƙara a Ukraine ta ce gawar mutum 1,222 aka gano a wani yanki na birnin Kyiv tun bayan da dakarun Rasha suka fice daga yankin.

Iryna Veneditktova ta faɗa kafar talabijin ta Sky News cewa hukumomin Ukraine na bincike kan lamura 5,600 da ake zargin an aikata laifukan yaƙi, kuma tuni ta iya tantance laifukan yaƙi 500, ciki har da wanda suka ƙunshi manyan jami’an sojan Rasha da na gwamnatin ƙasar.

“Abin da muke gani a yankunan Ukraine laifukan yaƙi ne, da laifuka kan ɗan Adamtakar mutane, kuma muna yin duk abin da za mu iya don magance hakan,” a cewarta.

Ta ce, Ukraine na da hujjar da ke nuna Rasha ta kai harin makami mai linzami kan tashar jirgin ƙasa a Kramatorsk da ke gabashin ƙasar, wanda ya kashe mutum fiye da 50 da ke jiran ƙarasowar jirgin.

Rasha ta musanta hannu a harin na ranar Juma’a tana mai iƙirarin cewa, ba makaminta ba ne. Ta kuma musanta kai wa fararen hula hari.

naija news legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...
X whatsapp