Hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Neja ta ce an gano gawawwakin mutum huɗu da wani hatsarin kwale-kwale ya rutsa da su a karamar hukumar Shiroro ta jihar Neja kwana hudu bayan faruwar lamarin.
Shugaban sashen yaɗa labarai da ayyuka na musamman na hukumar Ibrahim Audu ya sanar da hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar.
Jaridar Daily Trust dai ta ruwaito cewa wani jirgin ruwa ɗauke da mutum 34 ya kife a yammacin ranar Alhamis, inda mutum 10 suka mutu, yayin da aka ceto 24.
Fasinjojin waɗanda akasari ƴan kasuwa ne, sun haɗa da maza 20 da mata 14, daga cikinsu akwai yara mata takwas da manya mata shida.
Sai kuma yara maza biyu da manya maza 18.