Kwanaki uku bayan kashe wasu ma’aurata a jihar Ogun, an gano gawar ɗansu a cikin wani kogi a jihar.
Wasu mutane ne da ba a san ko su wane ne ba suka kashe ma’auratan masu suna Kehinde da Bukola Fatinoye a birnin Abeokuta na jihar a ranar sabuwar shekara bayan da suka dawo daga addu’o’in shiga sabuwar shekara.
Haka kuma rahotonni sun ce maharan sun ƙona gawarwakinsu da gidansu da ke birnin na Abeokuta, tare kuma da sace ɗan nasu inda kuma suka jefa shi cikin kogin.
An ce Kehinde ma’aikacin babban bankin Najeriya ne CBN, yayin da matar tasa ke aiki a jami’ar koyar da harkokin noma ta tarayya da ke Abeokuta.
Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar SP Abimbola Oyeyemi, rundunar na gudanar da bincike kan lamarin domin gano waɗanda suka aikata wannan mummunan aika-aika.