Gwamnan Jihar Gombe ya ce, Muhammadu Inuwa Yahaya, kamfanin NNPC ya gano danyen man fetur fiye da ganga biliyan 6 a yankin Kolmani da ke kan iyakar Gombe da Bauchi.
Inuwa Yahaya ya bawa mutanen jiharsa tabbacin cewa, ba zai yi kasa a gwiwa ba sai ya ga cewa an fara hakar man da iskar gas, domin jiharsa ta amfana.
Gwamnan ya ce rashin kudi da kuma annobar COVID-19 da ta janyo tsaiko a kasar ce ta sa aka jinkirta fara hako danyen man da iskar gas, amma zai cigaba da bibiyan batun.
Inuwa ya bayyana hakan ne yayin wata liyafa da aka shirya, domin karrama alkalin alkalai na wucin gadi na jihar Gombe, Hon Justice Muazu Abdulkadir Pindiga da aka yi a Pindiga a karamar hukumar Akko a ranar Asabar.
Ya ce, sau da yawa ya kai ziyara shelkwatar hukumar NNPC, kuma ya gana da shugaba Muhammadu Buhari, domin ganin yadda jiharsa za ta fara amfana da man fetur da iskar gas da ke jihar.