fidelitybank

An gano babbar masana’antar bama-bamai a wajen IPOB

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Ebonyi, ta ce, ta gano babbar masana’antar bama-bamai a yankin Kudu-maso-Gabas mallakar masu fafutukar kafa kasar Biafra, IPOB, da kuma Eastern Security Network, ESN.

Rundunar ‘yan sandan ta ce masana’antar bama-bamai ta IPOB/ESN ta kasance a Obegu da ke kan iyaka tsakanin Onicha-Isu da karamar hukumar Ishielu na jihar Ebonyi.

Kakakin rundunar ‘yan sandan, Chris Anyanwu, ya ce an gano masana’antar bam ne bayan an yi artabu da jami’an ESN.

Anyanwu ya ce masana’antar bama-bamai na da karfin haddasa kashe-kashe da barna.

Ya bayyana cewa ‘yan kungiyar ESN guda biyu da kwamandan jihar sun mutu a yayin artabu da ‘yan sanda da ake gudanar da bincike a kan hanyar Agba-Isu ranar Laraba.

Ya bayyana cewa wasu daga cikin ‘yan sandan sun samu raunuka a yayin samamen.

Ya kara da cewa, bayan fafatawar da aka yi da bindigar, tawagar hadin guiwa ta ’yan ta’adda ta Command’s Tactical Teams, Sojoji da DSS, dauke da sahihan bayanai, sun dira a gidaje/mazaunan Kwamandan da sauran su.

Kakakin rundunar ‘yan sandan ya ce binciken da aka gudanar a gidajen ya kai ga gano wasu na’urori masu fashewa da kuma sassan da ake amfani da su wajen kera bama-bamai.

A wata sanarwa da Anyanwu ya fitar na cewa: “An yi gaggawar tafiya tare da tawagar jami’an ‘yan sanda da ke aiki a sashin Ohaukwu, sun kama Sunday Ubah, aka Bongo, kwamandan IPOB/ESN na jihar Ebonyi.

“Kwararren dan sandan bama-bamai a cikin rundunar ya bayyana shi a matsayin cikakkiyar masana’antar bama-bamai – mafi girma a yankin Kudu-maso-Gabas kuma kowane nau’in bam na hannu (na farko) yana da ikon yin mummunar barna ga gine-gine da kuma kashe mutane. ”

A halin da ake ciki dai kungiyar ta IPOB ta sha musanta cewa tana da hannu a duk wani tashin hankali ko cinikin makamai.

www.legit.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp