fidelitybank

An gabatar da tuhume-tuhume takwas kan Ganduje – Muhuyi Magaji

Date:

Shugaban hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta jihar Kano, Muhuyi Magaji Rimin Gado ya ce sun suna yi wa tsohon gwamnan jihar Kano kuma shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Dr Abdullahi Umar Ganduje tuhume-tuhumen guda takwas.

A cewar Muhuyi tuhume-tuhumen sun haɗa da waɗnda suka danganci shigar kuɗi kimanin naira miliyan ɗari shida daga asusun gwamnatin Kano zuwa wani kamfani “wanda tsohon gwamna yake darakta a wajen sannan wanda yake tasarrafi da asusun mai ɗakinsa ce take yi”

Nan gaba a yau Laraba ne dai ake sa ran za a fara sauraron ƙarar da gwamnatin Kano ta shigar kan tsohon gwamnan jihar da iyalansa da wasu makusantansa bisa zargin cin hanci da rashawa da almundahana da dukiyar al’umma.

A na sa ran a gudanar da zaman fara sauraron shari’ar ne ƙarƙashin mai shari’a Usman Na’abba na babbar kotu mai lamba huɗu da ke jihar.

Shugaban hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta jihar Kano, Muhuyi Magaji Rimin Gado ya ce akwai ƙari cikin waɗanda ake ƙara da suka haɗa da mutum huɗu da wasu kamfanoni.

A cewarsa, sun shirya gabatar da shaidu 15 da za su gabatar gaban kotu saboda “mun samo hujja da ta danganta tsohon gwamna da laifuffuka da dokar hukuma ta haramta.”

Muhuyi Magaji ya ce akwai tuhume-tuhume takwas da suke yi kan tsohon gwamna Ganduje.

Sai dai wasu na ganin matakin gurfanar da tsohon gwamnan Kano da iyalinsa da hukumar yaƙi da rashawa ta jihar Kano ke yi masu yunƙuri ne na ramuwar gayya kan dakatarwar da Ganduje ya yi wa shugabanta – Muhuyi Magaji, zargin da ya musanta.

Ya bayyana cewa “shi ne dalilin da ya sa aka dakatar da ni tun farko, abu ne da muka fara shi tun yana gwamnati kuma ƴan jarida sun faɗa muna bincike kan wasu abubuwa da iyalinsa suke, kuma su ba su ƙaryata ba, babu wanda ya fito daga gwamnati ya ƙaryata,”

“Kuma abin da aka ce an dakatar da ni a kan shi, ba a iya tabbatar da shi ba har kotu ta ce mu dawo.” a cewar Muhuyi.

Ya ce akwai ƙarar da ke gabansu “wadda muka gano kuɗin ƙananan hukumomi, naira miliyan dubu 51 da miliyan 300.”

Game da wannan zargi na Muhuyi Magaji, lauyan tsohon gwamna Ganduje, Barista Musa Lawan ya ce ba za su halarci zaman kotun ba saboda har izuwa lokacin da BBC ta tattauna da shi, ya ce ba su samu takardar gayyata ba.

nnn hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...

Gwamnatin Tarayya za ta gina hanyar sufurin jirgin ƙasa a Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta samar da titin...

Abin da ya sa muke ci gaba da tsare Sowore – Ƴansanda

Kwamishinan ƴansanda mai kula da sashen kai ɗauki na...

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

Ɗaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi...

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...
X whatsapp