fidelitybank

An farmaki jami’an EFCC a Kaduna tare da rauna ta su

Date:

An kai wa jami’an EFCC hari a yayin da suke aikin sanya idanu a zaɓen da ake gudanarwa a na gwamnoni da ‘yan majalisun jihohi.

Cikin wata sanarwa da hukumar ta wallafa a shafinta na Facebook ta ce an kai wa jami’an nata hari ne a Unguwar Rimi yayin da suke yunƙurin kama wasu da ake zargi da sayen ƙuri’a.

Tawagar tasu da ke aikin sanya idanu na sirri ta yi zargin wani mutum da ake kira Kabiru Musa da aka gani cikin wani bidiyo riƙe da wayarsa yana aikawa mutane kudi idan suka kaɗa ƙuri’arsu, abin da ya sanya suka kai samamensu yankin ke nan domin su kama shi.

Da zuwansu suna ƙoƙarin kama shi, sai musa ya sanya ihu wanda tamkar alama ce ga abokan aikisa cewa yana cikin matsala.

Karanta Wannan: EFCC ta gurfanar da dan Indiya da zargin satar dala dubu 200

“Sun yi amfani da makamai kan jami’anmu abin da ya kai ga raunata wasunsu. Ya ɗauke su dogon lokaci suna fafatawa da matasan, saboda dagewar da suka yi sai sun kama wanda suke zargi.

“Bayan sun sanya wanda suke zargi a mota, sai aka fara jifan motar da manyan duwatsu da sauran abubuwa abin da ya sanya aka jikkata ma’aikatanmu uku kenan,” in ji sanarwar.

Waɗanda aka raunatan yanzu haka suna karɓar kulawa a wata cibiya da ke Kaduna, kuma wanda ake zargin yana hannu har zuwa a kammala bincike.

An kai wa ma’aikatan EFCC makamancin irin wannan hari a yayin zaɓen shugaban ƙasa da ya gudana, aka kuma lalata abun hawansu.

bbc news nigeria today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp