fidelitybank

An fara tantance adadin ƴan ƙasashen waje mazauna Kano da kasuwancin da su ke yi

Date:

Gwamnatin Kano ta fara tantancewa tare da yi wa ƴan ƙasashen waje mazauna jihar rajista da irin kasuwancin da suke yi.

An fara rajistar ne daga Kantin Kwari, domin tattara bayanan ƴan ƙasashen waje da suke zaune a jihar da sanin haƙiƙanin irin kasuwancin da suke yi.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa a jiya Laraba, wasu ƴan ƙasashen waje, musamman ƴan China da India sun je wajen rajistar domin a tantance su.

Sun kai takardu irin ru fasfo da sauran bayanansu, sannan wasu sun zo abokan kasuwancinsu ƴan jihar ta Kano domin tsaya musu.

Barista Tijjani Ahmed Falgore, wanda jami’i ne na ma’aikatar kasuwanci, wanda kuma yake cikin kwamitin rajistar, ya ce wasu ƴan ƙasashen wajen suna zaune ne a ƙasar ba tare da biyan haraji, wanda hakan ne ya sa aka ƙafa kwamitin.

“Maƙasudin shi ne a tantance daɗewarsu a ƙasar da kuma irin kasuwancin da suke yi a Kano,” in ji shi, sannan ya ƙara da cewa akwai sama da ƴan ƙasashen waje 6,000 a Kano.

An kafa kwamitin ne a ƙarƙashin Alhaji Lawal Isa Kibiya, wanda tsohon jami’in shigi da fice.

vanguard news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp