fidelitybank

An fara tantance adadin ƴan ƙasashen waje mazauna Kano da kasuwancin da su ke yi

Date:

Gwamnatin Kano ta fara tantancewa tare da yi wa ƴan ƙasashen waje mazauna jihar rajista da irin kasuwancin da suke yi.

An fara rajistar ne daga Kantin Kwari, domin tattara bayanan ƴan ƙasashen waje da suke zaune a jihar da sanin haƙiƙanin irin kasuwancin da suke yi.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa a jiya Laraba, wasu ƴan ƙasashen waje, musamman ƴan China da India sun je wajen rajistar domin a tantance su.

Sun kai takardu irin ru fasfo da sauran bayanansu, sannan wasu sun zo abokan kasuwancinsu ƴan jihar ta Kano domin tsaya musu.

Barista Tijjani Ahmed Falgore, wanda jami’i ne na ma’aikatar kasuwanci, wanda kuma yake cikin kwamitin rajistar, ya ce wasu ƴan ƙasashen wajen suna zaune ne a ƙasar ba tare da biyan haraji, wanda hakan ne ya sa aka ƙafa kwamitin.

“Maƙasudin shi ne a tantance daɗewarsu a ƙasar da kuma irin kasuwancin da suke yi a Kano,” in ji shi, sannan ya ƙara da cewa akwai sama da ƴan ƙasashen waje 6,000 a Kano.

An kafa kwamitin ne a ƙarƙashin Alhaji Lawal Isa Kibiya, wanda tsohon jami’in shigi da fice.

latest legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp