fidelitybank

An fara sayar da buhun shinkafa babba kan kudi dubu 40 a fadin kasar nan – Gwamnati

Date:

Gwamnatin Najeriya ta tabbatar wa ‘yan kasar cewa, an fara sayar da shinafa mai nauyin kilo 50 a kan kudi Naira 40,000 a sassan kasar nan.

Ministan yada labarai da wayar da kan jama’a na kasa, Mohammed Idris ne ya bayyana haka a lokacin da yake amsa tambayoyin ‘yan jarida yayin ganawa da manema labarai ranar Laraba a Abuja.

Ministan ya bayyana cewa an raba shinkafa a wuraren da aka kebe har zuwa lokacin da za a fara siyar da ‘yan Najeriya.

A cewarsa, gwamnati na ci gaba da bayyana hanyoyin da za a bi domin ganin cewa ba za a yi awon gaba da sayar da shinkafar da wasu mutane ba.

Ya kuma ba da tabbacin cewa gwamnati za ta bai wa ‘yan Najeriya cikakkun bayanai kan cibiyoyi a fadin kasar inda za su iya samun kayayyakin a kan wannan farashi.

“Zan iya tabbatar muku da cewa ana samun shinkafar kan Naira 40,000 kan kowace buhu mai nauyin kilo 50. Za a sayar da shi a cibiyoyi daban-daban a fadin kasar.

“Za mu ba ‘yan Najeriya cikakkun bayanai kan wuraren da aka siyar da su da zarar an fara siyar da su.

“Ana yin taka-tsan-tsan don kada wadanda ke da kudin saye da yawa su yi awon gaba da shi tare da yin amfani da wadanda ake so su samu,” in ji shi.

Bayanin na Ministan ya zo ne a daidai lokacin da ake ci gaba da nuna damuwa kan cewa har yanzu ba a samar da kayan a kasuwannin Najeriya kan Naira 40,000 kan kowacce buhu ba.

Idan za a tuna a ranar Litinin ne gwamnati ta sanar da rage farashin buhun shinkafa da kashi 50 zuwa N40,000 kan kowace buhu 50, yayin da ta yi kira ga ‘yan kasar da su guji zanga-zangar ranar 1 ga Agusta, 2024.

taraba news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp