fidelitybank

An fara ruwan farko a jihar Jigawa

Date:

Jihar Jigawa ta samu ruwan sama na farko a daminar shekarar 2023, inda aka samu saukin yanayin zafi.

Hakan ya ba mazauna yankin dadi sosai, bayan sun sha fama da zafi na tsawon wata daya da cizon sauro.

DAILY POST ta lura cewa mazauna yankin sun yi marhabin da ruwan sama cikin murna da annashuwa a kusan dukkan sassan jihar tare da fatan damina ta rage musu radadi.

Sai dai ruwan sama ya sha banban a wasu sassan jihar a yammacin Lahadi da dare wanda ya dauki tsawon mintuna 15 zuwa 30.

Malama Aisha, wata matar aure a garin Ringim ta ce ruwan sama ya sanyaya zafin da ake gani a yankin na tsawon lokaci.

“Tare da wannan ci gaban, yanzu muna kwana a gida cikin kwanciyar hankali ba tare da damu da yanayin zafi ba,” in ji ta.

Haka kuma, wasu daga cikin manoman da suka zanta da DAILY POST, sun bayyana jin dadinsu da wannan ci gaban.

Malam Abdullahi, wani karamin manomi a Dutse, ya ce duk da ruwan sama ya dan makara idan aka kwatanta da daminar bara, ya riga ya kwashe gonarsa yana jiran damina.

“Idan damina ta ci gaba a haka na tabbata nan da wasu kwanaki za mu fara dasa shuki cikin lokaci,” in ji shi.

Sai dai ya bukaci gwamnatoci da su shirya tunkarar damina tare da tallafa wa manoma tare da daukar matakan da suka dace domin kaucewa ambaliyar ruwa.

the nation newspaper 
today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp