Ana ci gaba da rushe harabar majalisar dokokin jihar Ribas.
Sama da katifila 10 ne ke ruguza ginin.
Gobara ta kone ginin a ranar 29 ga Oktoba, 2023.
‘Yan majalisar dokokin jihar 27 cikin 32 sun zargi kakakin majalisar Edison Ehie da wasu ‘yan majalisar uku da hannu a tashin gobarar.
Hakan ya sa aka dakatar da Ehie da wasu uku daga Majalisar a ranar 30 ga Oktoba, 2023.
Sai dai a wani zama na daban, Ehie ya fito a matsayin kakakin majalisar ya kuma dakatar da Martins Amaewhule a matsayin shugaban majalisar, tare da wasu ‘yan majalisar da ya ki bayyana sunayensu.
A ranar Talata 12 ga Disamba, 2023, wata babbar kotun jihar Ribas da ke zama a Fatakwal ta ayyana Ehie a matsayin sahihin shugaban majalisar.
Rikicin da ya barke a majalisar dokokin jihar Ribas na da nasaba ne da rashin jituwar da ke tsakanin gwamna Siminalayi Fubara da ministan babban birnin tarayya (FCT), Nyesom Wike.