fidelitybank

An fara rushe harabar majalisar dokokin jihar Ribas

Date:

Ana ci gaba da rushe harabar majalisar dokokin jihar Ribas.

Sama da katifila 10 ne ke ruguza ginin.

Gobara ta kone ginin a ranar 29 ga Oktoba, 2023.

‘Yan majalisar dokokin jihar 27 cikin 32 sun zargi kakakin majalisar Edison Ehie da wasu ‘yan majalisar uku da hannu a tashin gobarar.

Hakan ya sa aka dakatar da Ehie da wasu uku daga Majalisar a ranar 30 ga Oktoba, 2023.

Sai dai a wani zama na daban, Ehie ya fito a matsayin kakakin majalisar ya kuma dakatar da Martins Amaewhule a matsayin shugaban majalisar, tare da wasu ‘yan majalisar da ya ki bayyana sunayensu.

A ranar Talata 12 ga Disamba, 2023, wata babbar kotun jihar Ribas da ke zama a Fatakwal ta ayyana Ehie a matsayin sahihin shugaban majalisar.

Rikicin da ya barke a majalisar dokokin jihar Ribas na da nasaba ne da rashin jituwar da ke tsakanin gwamna Siminalayi Fubara da ministan babban birnin tarayya (FCT), Nyesom Wike.

nhgsfp

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp