fidelitybank

An fara dogon layin man fetur a Abuja

Date:

Dogayen layukan sayen mai sun sake bayyana a Abuja, babban birnin tarayya, abin da ya jefa masu motoci cikin damuwa.

Tun daga ranar Talata ne matsalar ta sake bayyana wadda daman brnin ya yi fama da ita a cikin shekarar nan, lamarin da ya sa masu ababan hawa ke kokawa a kan matsalar.

Ana iya ganin dogayen layukan motoci a wasu gidagen sayar da mai biyu da ke daura da hedikwatar kamfanin mai na Najeriya a tsakiyar birnin na Abuja.

Sakamakon karancin man masu sayar da shi a gefen titi, a jarkoki sun sake bayyana a manyan titunan cikin birnin, inda suke sayar da galan mai cin lita 10 a kan Naira 2,500 zuwa 3,000.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa wani mai mota, mai suna Umar da ta yi hira da shi ya ce ya sayi man a kan Naira 300 lita daya a wajen babban birnin.

Hukumomin Najeriya sun ce ambaliyar ruwa da ta auku a hanyar Lokoja ce ta sa jinkirin motocin dakon mai zuwa arewacin Najeriya daga Lagos da sauran wuraren da ake dauko man.

Wata kungiyar masu dakon man kuma ta ce lalacewar hanyar jihar Naija ma ta kara ta’azzara matsalar sufurin man zuwa arewacin Najeriyar.

nigerian 
news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp