fidelitybank

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Date:

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya fashe a jihar Kano, wanda ya yi sanadiyar mutuwar aƙalla mutum, sannan wasu mutum 15 suka jikkata.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa lamarin ya auku ne a ranar Asabar, wanda ya jefa tsoro da fargaba a yankin da ya faru.

Kwamishinan ƴansandan jihar Kano, Ibrahim Adamu Bakori, wanda ya ziyarci wajen jim kaɗan bayan fashewar, ya ce abin suna tunanin fashewar daga wata mota ce da ta taso daga jihar Yobe.

“Da aka kira sai na tafi wajen cikin gaggawa, da na isa sai na fahimci cewa wani abu ne – wataƙila bom ne – ya fashe. Aƙalla mutum 5 sun rasu, sannan 15 suka jikkata,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa, “mun fara bincike asalin musabbabin aukuwar lamarin, amma muna tunanin motar da ta ɗauko abin fashewar daga jihar Yobe take.

“Binciken farko-farko ya nuna cewa wata motar tirela ce ta kwaso wasu abubuwa masu fashewa. Amma zuwa yanzu ba mu da tabbacin ko kayan sojoji ne, ko na kuma ta ƴan kwangila,” in ji shi.

“Amma za mu fayyace komai da zarar mun kammala bincike.”

legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

QPC ta nemi INEC ta soke zaɓen Kano

Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya ta nemi hukumar zaɓe...

Zaɓen Kano: An kama Mutane 288 da tayar da zaune tsaye

Rudunar ƴansandan jihar Kano, ta sanar da kama mutum...

An Kama wakilin jam’iyya da Naira miliyan 25.9 na Siyan Kuri’a

Jami’an tsaro sun kama wani da ake zargin wakilin...

Farashin kayan abinci na rugu-rugu a Najeriya – NBS

Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS) ta ce hauhawar farashin...

Kotun Kano ta ce a kamo mata Dagacin Tamburawa

Kotun Shari’ar Musulunci da ke shelkwatar Hisbah a Kano,...

Kotu ta ƙwace motocin gwamnatin Zamfara guda 40 daga hannun Matawalle

Kotun Daukaka Kara da ke a Sokoto ta tabbatar...

A na cigaba da gudanar da zaben cike gurbi harda Kano

Kano na ɗaya daga cikin jhihohin da ake kaɗa...

Mutane 12 sun mutu a wani hatsari a Kano – FRSC

Hukumar Kiyaye Haddura ta Ƙasa (FRSC) reshen Kano, ta...

Masarutar Rano ta haramta aurar da Yaran da ba su kammala karatun Firamare ba

Masarautar Rano a Kano ta haramta cire yarinya daga...

Matatar Dangote za ta fara jigilar mai kyauta ga gidajen mai

Matatar man Dangote za ta fara jigilar mai kyauta...

An sassata rikicin da aka shafe shekaru 30 kan Masallacin Sharada da Islamiyya

Tsohon dan takarar gwamnan Kano, Malam Sha’aban Ibrahim Sharada,...

Duk da kalubalen ‘yan siyasa a Kano mun shirya a zaben cike gurbi – INEC

Kwamishinan hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) reshen jihar...
X whatsapp