Hukumomi a karamar hukumar Wudil a jihar Kano na cewa, jami’an tsaro suna ci gaba da kwato kayayyakin da wasu bata-gari suka sace a sakatariyar karamar hukumar lokacin zanga-zangar da ta rikide zuwa tarzoma.
Baya ga sace-sacen da aka yi a cikin birnin Kano cikin kananan hukumomin jihar arba’in da hudu Wudil ce lamarin tarzomar ya fi muni inda ake cewa an sace dukiya ta miliyoyin naira.
Shugabar karamar hukumar, Hajiya Bilkisu Yakubu, ta shaida wa BBC cewa, ba su da ofishoshin da za su yi aiki saboda an lalata tare da kona sakatariyar karamar hukumar.
Shugabar ta ce jami’an tsaro suna nan suna gudanar da bincike, tare da kwato wasu daga cikin kayayyakin.
Ta kara da cewa ba wai kayan gwamnati kadai aka washe ba, har ma da wasu kayayyakin na ‘yan kasuwa da sauran jama’a da aka sace.
Hajiya Bilkisu ta ce, ko kadan ba za su iya kiyasin yawan asarar da aka tafka ba a dalilin abin da masu zanga-zangar suka yi.
Haka kuma ta ce, babu wasu da za a iya fitowa fili a zarga da aikata wannan ta’asa, illa dai ta ce bincike zai gano kamar yadda jami’na tsaro suka lashi takobi, ganin yadda suke bi suna kwato wasu daga cikin abubuwan da aka sace.