fidelitybank

An fara ƙwato kayan abincin da aka sace a Wudil – Shugabar Ƙaramar Hukuma

Date:

Hukumomi a karamar hukumar Wudil a jihar Kano na cewa, jami’an tsaro suna ci gaba da kwato kayayyakin da wasu bata-gari suka sace a sakatariyar karamar hukumar lokacin zanga-zangar da ta rikide zuwa tarzoma.

Baya ga sace-sacen da aka yi a cikin birnin Kano cikin kananan hukumomin jihar arba’in da hudu Wudil ce lamarin tarzomar ya fi muni inda ake cewa an sace dukiya ta miliyoyin naira.

Shugabar karamar hukumar, Hajiya Bilkisu Yakubu, ta shaida wa BBC cewa, ba su da ofishoshin da za su yi aiki saboda an lalata tare da kona sakatariyar karamar hukumar.

Shugabar ta ce jami’an tsaro suna nan suna gudanar da bincike, tare da kwato wasu daga cikin kayayyakin.

Ta kara da cewa ba wai kayan gwamnati kadai aka washe ba, har ma da wasu kayayyakin na ‘yan kasuwa da sauran jama’a da aka sace.

Hajiya Bilkisu ta ce, ko kadan ba za su iya kiyasin yawan asarar da aka tafka ba a dalilin abin da masu zanga-zangar suka yi.

Haka kuma ta ce, babu wasu da za a iya fitowa fili a zarga da aikata wannan ta’asa, illa dai ta ce bincike zai gano kamar yadda jami’na tsaro suka lashi takobi, ganin yadda suke bi suna kwato wasu daga cikin abubuwan da aka sace.

nigerian 
newspapers today the sun

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp