fidelitybank

An dawo wa da Alhazan Kano kudin aikin Hajjin 2023 sama da Naira miliyan 375

Date:

Babban Daraktan Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kano, Alhaji Lamin Rabi’u Danbappa, ya sanar da mayar da sama da Naira miliyan 375,397,680 ga maniyyatan Jihar Kano da suka halarci aikin hajjin 2023.

Da yake jawabi yayin wani taron gudanarwa da aka gudanar a ofishinsa, Alhaji Lamin Rabi’u ya bayyana cewa hukumomin Saudiyya ne suka ware wadannan kudade ta hannun hukumar alhazai ta kasa (NAHCON) a matsayin diyya ga matsalar wutar lantarki da aka samu a Mina a lokacin aikin hajji.

Alhazai 6,146 ne daga jihar Kano suka shiga aikin Hajjin shekarar 2023, inda kowannensu ya karbi Naira 61,080.

A cewar Sulaiman A. Dederi, jami’in hulda da jama’a na hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kano, an tsara tsarin raba kudaden ne domin tabbatar da gaskiya da rikon amana.

Ya bayyana cewa za a tura dukkan kudaden da za a biya kai tsaye zuwa asusun ajiyar alhazai na banki, tare da kawar da duk wani sabani.

Ya kuma kara tabbatar wa da jama’a cewa hukumar ta jajirce wajen ba da fifiko ga jin dadin alhazai da kuma kula da ingancin hidima.

Babban Darakta ya karfafa jami’an cibiyar alhazai na kananan hukumomi da su kara kaimi wajen inganta siyar da kujerun aikin hajjin da za a yi.

Ya nuna damuwarsa kan yadda ake tafiyar hawainiya wajen sayar da kujerun, sannan ya bukaci a hada kai don tabbatar da gudanar da ayyuka masu inganci da kuma inganta ayyukan hidima ga mahajjata.

daily sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp