Babban Daraktan Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kano, Alhaji Lamin Rabi’u Danbappa, ya sanar da mayar da sama da Naira miliyan 375,397,680 ga maniyyatan Jihar Kano da suka halarci aikin hajjin 2023.
Da yake jawabi yayin wani taron gudanarwa da aka gudanar a ofishinsa, Alhaji Lamin Rabi’u ya bayyana cewa hukumomin Saudiyya ne suka ware wadannan kudade ta hannun hukumar alhazai ta kasa (NAHCON) a matsayin diyya ga matsalar wutar lantarki da aka samu a Mina a lokacin aikin hajji.
Alhazai 6,146 ne daga jihar Kano suka shiga aikin Hajjin shekarar 2023, inda kowannensu ya karbi Naira 61,080.
A cewar Sulaiman A. Dederi, jami’in hulda da jama’a na hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kano, an tsara tsarin raba kudaden ne domin tabbatar da gaskiya da rikon amana.
Ya bayyana cewa za a tura dukkan kudaden da za a biya kai tsaye zuwa asusun ajiyar alhazai na banki, tare da kawar da duk wani sabani.
Ya kuma kara tabbatar wa da jama’a cewa hukumar ta jajirce wajen ba da fifiko ga jin dadin alhazai da kuma kula da ingancin hidima.
Babban Darakta ya karfafa jami’an cibiyar alhazai na kananan hukumomi da su kara kaimi wajen inganta siyar da kujerun aikin hajjin da za a yi.
Ya nuna damuwarsa kan yadda ake tafiyar hawainiya wajen sayar da kujerun, sannan ya bukaci a hada kai don tabbatar da gudanar da ayyuka masu inganci da kuma inganta ayyukan hidima ga mahajjata.