fidelitybank

An dawo da ƴan Najeriya da aka yi safararsu zuwa Ghana

Date:

Hukumar Kula da ‘yan Najeriya mazauna ƙetare NIDCOM, ta ce an mayar da ‘yan matan ƙasar kimanin 10 da aka yi safararsu zuwa Ghna.

Cikin wata sanarwa da shugabar hukumar, Abike Dabiri-Erewa ta wallafa a shafinta na X, ta ce a ranar Juma’a ne ‘yan matan waɗanda aka kuɓutar daga Ghana suka koma ƙasar.

Ta ce ‘yan matan – waɗanda mafi yawansu ‘yan jihar Imo ne – na tare da wakilan gwamnatin jihar.

Ms Dabiri ta ce hukumarta ta samu bayanan ‘yan matan ne daga hukumar yaƙi da safarar bil-adama ta ƙasar (NAPTIP).

‘Yan matan – waɗanda dukansu ‘yan ƙasa da shekara 18 ne – wani mutum ne da ba a ambaci sunansa ba ya yi safararsu zuwa Ghana.

Tuni dai ‘yan sanda Ghana suka cafke mutumin, inda suke ci gaba da gudanar da bincik.

Ms Dabiri kungiyar ‘yan Najeriya mazauna ƙetare reshen ƙasar Ghana ne suka taimaka wajen kuɓutar da yaran.

today nation

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp