fidelitybank

An daure Matasan da suke kalaman batsa ta cikin Tiktok a Kano

Date:

Wata kotun majistre mai zama a Norman’s land da ke karamar hukumar Fagge na jihar Kano, ta ɗaure wasu masu amfani da shafin TikTok biyu a gidan yari, bayan samunsu da laifin amfani da bidiyo mai ɗauke da kalaman batsa.

Hukumar tace fina-finai ta jihar ta kama mutanen ne Ahmad Isa da Maryam Musa mazauna anguwar Ladanai da ke Hotoro Quarters, inda daga bisani ta miƙa su ga kotun, kamar yadda Jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Lauyan gwamnatin jihar ta Kano, Barrister Garzali Maigari Bichi, ya same su da aikata laifi da ya kunshi haɗa baki don aikata laifi da kuma wallafa hotunan bidiyo masu ɗauke da kalaman batsa a shafukan sada zumunta.

Mutanen biyu sun amsa aikata laifin.

Alkaliyar kotun, mai shari’a Hadiza Muhammad Hassan ta yanke musu hukuncin zama gidan yari na shekara ɗaya ko kuma biyan tarar naira 100,000 kowannensu – ta hore su da su zama mutanen kirki.

latest news 
in nigeria today 2021 punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp