Wata kotun majistre mai zama a Norman’s land da ke karamar hukumar Fagge na jihar Kano, ta ɗaure wasu masu amfani da shafin TikTok biyu a gidan yari, bayan samunsu da laifin amfani da bidiyo mai ɗauke da kalaman batsa.
Hukumar tace fina-finai ta jihar ta kama mutanen ne Ahmad Isa da Maryam Musa mazauna anguwar Ladanai da ke Hotoro Quarters, inda daga bisani ta miƙa su ga kotun, kamar yadda Jaridar Daily Trust ta ruwaito.
Lauyan gwamnatin jihar ta Kano, Barrister Garzali Maigari Bichi, ya same su da aikata laifi da ya kunshi haɗa baki don aikata laifi da kuma wallafa hotunan bidiyo masu ɗauke da kalaman batsa a shafukan sada zumunta.
Mutanen biyu sun amsa aikata laifin.
Alkaliyar kotun, mai shari’a Hadiza Muhammad Hassan ta yanke musu hukuncin zama gidan yari na shekara ɗaya ko kuma biyan tarar naira 100,000 kowannensu – ta hore su da su zama mutanen kirki.