fidelitybank

An daure Basarake da mutane 14 bisa harkallar filaye

Date:

Wata babbar kotun jihar Oyo da ke zamanta a Ogbomoso, ta tasa keyar daya daga cikin sarakunan gargajiya a jihar zuwa gidan gyaran hali.

Rahotanni na cewa an tsare basaraken, Oloko na Oko, Oba Solomon Akinola, da wasu mutane 14 a gidan yari na Abolongo.

An tsare su ranar Laraba bisa zargin ci gaba da kai hare-hare, yunkurin kisan kai, da kuma kwace filaye.

Justice K.A. Adedokun ya ba da umarnin ne a lokacin da lauyan jihar, I. O. Abdulazeez, ya shaida wa kotun cewa wadanda ake kara sun sake kai wa mai karar Dokta Isaac Abiodun hari a kauyen Aagba.

Wadanda kotun ta tsare baya ga basaraken sun hada da Cif Sunday Aderinto, Cif Jimoh Asimiyu, Timothy Aderinto, Matthew Akintaro, Rafiu Ganiu, da Adejare Adeleru.

Sauran sun hada da Samson Ogunmola, Zachiaus Adeleru, Kamorudeen Ajibade, Raji Rasaq, Mutiu Arowosaye, Oyeyemi Oyelekan, Olusegun Oyelekan, da Sheriff Adio.

Mai shari’a Adedokun, yayin da yake magana, ya fusata kan sabon harin ta’addancin da aka kai wa Abiodun.

Alkalin kotun ya bayar da umarnin a ci gaba da tsare wadanda ake tuhuma sannan ya dage sauraron karar zuwa ranar 27 ga watan Nuwamba domin sauraren neman beli.

vanguard newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp