fidelitybank

An dauke wutar lantarki a fadar Tinubu

Date:

Babban birnin tarayyar Najeriya, Abuja ya gamu da matsalar ɗaukewar wutar lantarki sakamakon lalacewar wasu layikan da ke kai lantarkin sassan birnin na kamfanin da ke samar da wutar (AEDC) ya sanar.

Hatta fadar gwamnatin ƙasar matsalar ɗaukewar wutar ta shafa kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito a yau Juma’a.

Kamfanin samar da lantarkin (AEDC) a wata sanarwa da ya rinƙa fitarwa akai-akai a shafinsa na X, ya roƙi masu amfani da wutar da su yi haƙuri, yayin da ya ce ma’iakatansa na aiki tuƙuru domin shawo kan matsalar, don mayar da wutar ga sassan da abin ya shafa.

To amma daman wasu unguwannin wajen birnin kamar su Lugbe da Kubwa daman sun yi kwanaki ba su da wutar lantarkin.

A sanarwar da kamfanin ya fitar ya ambato unguwanni da yankuna da dama da matsalar ta shafa.

A jiya Alhamis aka ruwaito ministan makamashi, Adebayo Adelabu, a lokacin gabatar da shiri da manufar gwamnatin ƙasar kan samar da lantarki ya nuna takaicinsa kan ci gaba da lalacewar kayan samar da lantarki a ƙasar.

Ministan ya ɗora alhakin hakan a kan rashin aniyar kamfanonin rarraba lantarkin ta zuba jari a harkar.

daily post nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp