Babban birnin tarayyar Najeriya, Abuja ya gamu da matsalar ɗaukewar wutar lantarki sakamakon lalacewar wasu layikan da ke kai lantarkin sassan birnin na kamfanin da ke samar da wutar (AEDC) ya sanar.
Hatta fadar gwamnatin ƙasar matsalar ɗaukewar wutar ta shafa kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito a yau Juma’a.
Kamfanin samar da lantarkin (AEDC) a wata sanarwa da ya rinƙa fitarwa akai-akai a shafinsa na X, ya roƙi masu amfani da wutar da su yi haƙuri, yayin da ya ce ma’iakatansa na aiki tuƙuru domin shawo kan matsalar, don mayar da wutar ga sassan da abin ya shafa.
To amma daman wasu unguwannin wajen birnin kamar su Lugbe da Kubwa daman sun yi kwanaki ba su da wutar lantarkin.
A sanarwar da kamfanin ya fitar ya ambato unguwanni da yankuna da dama da matsalar ta shafa.
A jiya Alhamis aka ruwaito ministan makamashi, Adebayo Adelabu, a lokacin gabatar da shiri da manufar gwamnatin ƙasar kan samar da lantarki ya nuna takaicinsa kan ci gaba da lalacewar kayan samar da lantarki a ƙasar.
Ministan ya ɗora alhakin hakan a kan rashin aniyar kamfanonin rarraba lantarkin ta zuba jari a harkar.