fidelitybank

An damke mutumin da ya kashe matarsa da wuka a Yobe

Date:

Rundunar ƴan sandan Yobe ta kama wani magidanci mai shekara 43 kan zarginsa da hannu a mutuwar matarsa mai shekara 42.

Kakakin rundunar ‘yansandan jihar DSP Dungus Abdulkarim ya tabbatar wa BBC faruwar lamarin wanda ya ce suna kan gudanar da bincike kan lamarin.

DSP Dungus ya ce mutumin na tare da matarsa a ɗakinsu a lokacin da aka soke ta a wuya, lamarin da ya sa ta yi ta zubar da jini har rai ya yi halinsa.

Lamarin ya faru ne a Damaturu bayan da al’ummar rukunin gidajen New Bra Bra suka tashi da labarin mai ratsa zuciya bayan gano gawar matar yashe a gidanta da yanka a wuyanta.

mai magana da yawun ‘yansandan ya ce rundunar ta fara gudanar da bincike game da mummunan lamarin domin gano mutanen da suke da hannu.

Ya kara da cewa duka da cewa yankan bai kai ga makogoron matar ba, amma ya shafi jijiyoyin da ke kai jini zuwa kanta, ta yada babu yadda za a yi ta rayu.

Ya kuma ce kawo yanzu bincikensu bai gano abin da aka yanka ta da shi ba.

A cewar rundunar, ma’auratan ma’aikata ne a jami’ar jihar Yobe da ke Damaturu.

vanguard new

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp