fidelitybank

An damke mutane 13 da hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba a Kwara

Date:

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arziki Tu’annati (EFCC) tare da hadin guiwar Hukumar Tsaro da Civil Defence na Jihar Kwara (NSCDC) da Hukumar Kula da Ma’adanai da Karfe ta Tarayya, sun kama wasu mutane 13 da ake zargin masu hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba ne da ke aiki a kauyen Kakafu a Karamar hukumar Patgi dake jihar Kwara.

Wadanda ake zargin, kamar yadda binciken THISDAY ta rawaito, an kama su ne a ranar Talatar da ta gabata a wani samame na hadin gwiwa.

An tattaro cewa an samu nasarar cafke shi ne biyo bayan sahihan bayanan sirri da hukumar EFCC ta samu kan wasu da ake zargin masu hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba ne da ke gudanar da ayyukansu a yankin.

Idan dai za a iya tunawa, rundunar shiyar Ilorin na EFCC da NSCDC a jihar Kwara a ranar Alhamis din da ta gabata ta kara zage damtse wajen yaki da hako ma’adinai ba bisa ka’ida ba a jihar.

Wata sanarwa da aka fitar jiya a Ilorin mai dauke da sa hannun jami’in hulda da jama’a na hukumar tsaro ta farin kaya, Mista Olasunkanmi Ayeni, ta bayyana cewa: An kama wadanda ake zargin sun hada da, Buba Mohammed, Yusuf Umar, Surajo Shehu, Abubakar Abdullahi, Salisu Mohammed, Quadri Sulaiman. da Nwafor Chinonso.

“Sauran su ne: Abdullahi Isa, Mustapha Mohammed, Buhari Hassan, Basiru Jafaru, Murtala Jafaru da Jafaru Abdullahi.”

Sanarwar ta kara da cewa, an samu nasarar kwato manyan motoci biyar cike da ma’adanai daban-daban daga hannun wadanda ake zargin.

“Bincike na farko ya nuna cewa wadanda ake zargin ba sa biyan gwamnatin tarayya hakkokinsu kamar yadda doka ta tanada.”

Sai dai sanarwar ta bayyana cewa: “Ba da jimawa ba za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu bayan kammala binciken da ake yi.”

punch news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...
X whatsapp